Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya samu babbar karramawa a matakin ƙasa da ƙasa bayan da aka ba shi lambar yabo ta “Gwamnan ...
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya samu babbar karramawa a matakin ƙasa da ƙasa bayan da aka ba shi lambar yabo ta “Gwamnan Shekara” a bikin Fuskar Jagoranci a Afirka 2026, wato Face of Africa Leadership Award 2026, da aka gudanar a birnin Landan.
Wannan karramawa ta fito ne daga mujallar duniya ta Triangle Media International Magazine, wadda ke karrama fitattun shugabanni daga sassa daban-daban na duniya bisa irin tasirin da suke da shi a shugabanci da hidimar jama’a.
An gudanar da taron karo na goma na wannan muhimmin biki a babban zauren King’s College da ke Landan, inda manyan baƙi daga bangarorin gwamnati da masu zaman kansu suka halarta domin tattauna muhimmancin rawar da ‘yan Nijeriya mazauna ƙasashen waje ke takawa wajen bunƙasa ci gaban ƙasa.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya bayyana cewa wannan lambar yabo ta 2026 ta zo ne daidai lokacin da mujallar ke bikin cika shekaru goma da kafuwa, tare da ci gaba da karrama fitattun ’yan Afirka masu tasiri.
Sanarwar ta jaddada cewa an ba Gwamna Lawal wannan karramawa ne bisa irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu tun bayan rantsar da shi a ranar 29 ga Mayu, 2023, musamman a bangaren inganta ayyukan gwamnati da hidimar jama’a.
Kwamitin masu ba da kyautar ya bayyana cewa duk da halin matsin tattalin arziki da gwamnatin ta gada, Gwamna Lawal ya tsaya tsayin daka wajen aiwatar da manufofin “Ƙudurin Ceto” domin farfaɗo da jihar Zamfara.
Haka kuma, an yaba da dabarun da gwamnatin ke bi wajen rage matsalolin tsaro ta hanyar saka jari a fannin ilimi, ciki har da ayyana dokar ta-ɓaci a bangaren ilimi, da kuma biyan bashin kuɗaɗen jarrabawar WAEC da NECO da suka kai Naira biliyan 3.4.
Bugu da ƙari, an nuna yadda gwamnatin ta mayar da hankali wajen gyara da sake gina makarantu a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar, wanda aka bayyana a matsayin mataki mai muhimmanci wajen tabbatar da ci gaba mai ɗorewa.
Taron ya samu halartar manyan baƙi ciki har da Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, da Babban Daraktan Kamfanin Sahara Group, Kola Adesina, tare da sauran fitattun mutane.
Wannan karramawa na ƙara tabbatar da matsayin Gwamna Lawal a matsayin ɗaya daga cikin shugabannin da ke kawo sauyi a Nijeriya, tare da ƙarfafa gwiwar gwamnatinsa wajen ci gaba da ayyukan ci gaba a jihar Zamfara.
No comments